Wannan addu'ar ana yin ta domin neman biyan bukata a wajen Allah (T) kuma tana da matukar tasiri ga yadda bayanin addu'ar take kamar haka:
ALLAH a cikin AlÆ™ur'ani an Æ™ira Shi da "Ø£َرْØَÙ…ُ الرّاØِمین" sau huÉ—u, kuma duk sun zo ne a yayin siffanta ALLAH É—in. Yin zikirinta bayan ka ambaci "یا" a Æ™alla sau bakwai yana kaiwa ga biyan buÆ™ata. Yawan ambatan "یا رØÙ…ان" yana sauyawa mutum hali daga mai kaushin zuciya zuwa mai taushin zuciya.
Annabi Ayuba A.S ya kira ALLAH da "Ø£َرْØَÙ…ُ الرّاØِمین" bayan ya ambaci irin halin da yake ciki na matsaloli da damuwa. Kun san yadda ya talauce, ya rasa Æ´aÆ´a da duk wani abu da ALLAH Ya mallaka masa, amma bai bari ya rasa harshe da zuciya don ambatan Ubangijinsa ba. To duk wani mai tsananin damuwa idan ya lizimci wannan, zai samu mafita.
Bayan sunan ALLAH, da siffarsa ar-Rahman (mai rahma), akwai Siffofinsa irinsu: Ya Rahim; Ya mai Jin Ƙai, Ya Karim; Ya Mai Karamci, Ya Muƙim; Ya Mai Tsayarwa (kamar tsayuwar da sama), Ya Azimu; Ya Mai Girma, Ya Ƙadimu; Ya Daɗaɗɗe, Ya Alimu; Ya Masani, Ya Halimu; Mai Haƙuri da jinkiri, Ya Hakimu; Mai Hikima.
Yin Tawassuli da waɗannan sunaye da siffofin, yana sanya mutum samun kusanci da ALLAH da kuma biyan buƙata.